(((((((((Boyayyar Taska))))))) Sai ya yi nadama kamar yadda - TopicsExpress



          

(((((((((Boyayyar Taska))))))) Sai ya yi nadama kamar yadda Tarihi ya kawo, daga nan kuma sai ya zama shi ne mai fada a ji a Addinin, ya kori Hawariyawada Wasiyyai (A.S) aka kashe na kashewa aka kore na kore wa zuwa dazuka da tsaunuka, sannan kuma yawancin Akidu na asasin Kiristanci daga koyarwarsa ne, Mabiyansa suka yawaita, ya ci gaba da bin ragowar Hawariyawa da muminai da suka yi lokaci daya da Annabi Isa (A.S) har sai da suka kare. Wani abin mamaki shi ne, ina sauran al’umma suke da zasu yarda da makiyin da ya zo ya gane gaskiya har zai zama ra’ayoyinsa su ne daidai game da Addini da za a bar na WasiyyanIsa (A.S). Bayan Fiyayyen Halittu Manzo (S.A.W) Haka nan Tarihi ya rubata mana rikici da sabanida suka wakana bayan wafatin Manzon Allah (S.A.W) har ya zamanto ba wanda ya halarci jana’izar fiyayyen halittu sai Sayyidi Ali (A.S) da wasu daga sahabbansa, amma sauran al’umma sunacan suna jayayya a kan waye zai zama halifa!, alhali ga shi ba a ma binne shi ba!. Sai al’umma ta shiga sabani wasu sunacewa: Halifanci na Ali ne domin shi aka yi wasiyya da shi, kamar hadisin wasiyya ko hadisud-dar, da hadisin manzila, da hadisin Gadir khum, har ma an yi wa Imam Ali (A.S) bai’a a ranar Gadir wacceba ta wuce wata biyu ba kafin rasuwar manzon Allah (S.A.W)[5], saboda haka ba wanda zasu yi wa bai’a sai Ali (A.S). Wasu jama’a suna ganin a bar al’amarin ya zama tsakanin kuraishawa suna musaya da fasin da halifanci kamar yadda ake yi da kwallo. Rigima a Sakifa ta kai ga zare takobi amma Allah ya sa ba a zubar da jini ba, har abin ya kai ga Umar dan Khaddabida wasu daga Ansar da ba sa shiri da Sa’ad Dan Ubbad suka yi bai’a ga Abubakar Dan Abi Kuhafa a matsayin halifan Manzo (S.A.W), daga nan ne suka bar Sakifa zuwa wajanda akezaman juyayi da makoki na Manzo Allah (S.A.W), aka kuma tayar da wani rikici a wajan tsakanin musulmi, al’amarin abin sanya kuka ne a tayar da hayaniya a wajan makokin Manzo (S.A.W), har da zare takobi wani daga jama’a yana nuna takubi ga wuyanmasu zaman makoki yana ku tashi ku yi bai’a! Amma Ahlul Bait (A.S) daidai da rana daya ba su taba yarda da bai’ar halifa na farko ba, ruwayoyi suna cewa: Sayyidi Ali (A.S) bai yi bai’a ba sai bayanwafatin Zahra (A.S) shi ma bisa tilas, ya daga hannunsa ya buga kan na halifan musulmi[6]. Ahlul Baiti (A.S) sun ki yarda da halifancin wani wanda ba Imam Ali ba suna masu dogaro da da hujjar cewa; Manzon Allah (S.A.W) ya yi wasiyya ga Ali (A.S) tun yana raye. Imam Ali (A.S) da mabiyansajama’ar muminai mabiya wasiyyar Manzo da aka fi sani da Shi’ar Ali ko Shi’ar Ahlul Baiti (A.S) ba su yi bai’a ba har bayan wafatin Fadima (A.S) bayan sun ga cewa idan ba su yi ba to za a kashe suko a kona gidajensu. Wanda ya fi kowa tsanantawa kan halifan farko daga Ahlul Baiti (A.S) ita ce Fadima (A.S) har ma ta yi fushi da halifa na farko da na biyu, ta kuma yi fushi da su ba ta kara yi musu magana ba, kuma ta yi alkawarin yi musu addu’a a kowace salla, da kuma kai su kara wajan Annabi (S.A.W), haka nan har ta mutu ba ta kara kallon su ko yi musu magana ba kamar yadda ya zo a Littafin Sahihul Bukhari, da Imama wassiyasa, kuma ta yi wasiyya ga Imam Ali (A.S) da idan ta mutu kada wani ya halarci kabarinta daga al’ummar Manzo (S.A.W) sai Shi da ‘Ya’yanta da wasu mutune da ba su wuce biyu ba. Wannan al’amarin ya jawo har yanzu ba wanda ya san kabarinta a nan Madina, wani abin mamaki shi ne ba ma mai tambayar kabarinta dagaal’ummar musulmi ko dalilin da ya sa ba a san inda yake ba. Wannan ya sanya har yanzu kowa yana da kabari da za a yi nuni zuwa gareshi amma banda Fadima ‘yar Annabin wannan al’umma (A.S) har yanzu babu wanda ya san kabarinta, Tarihi yana cewa: Idan Imam Mahadi (A.S) ya bayyana shi ne zai nuna kabarin nata. Su Waye Wasiyyan Annabi (A.S) Ahlul Baiti (A.S) da mabiyansu sun imani da cewar Manzo rahama ya yi wasiyya ga mutum goma sha biyu a bayansa wadanda su ne halifofinsa, haka ma Ahlussunna sun tafi a kan Manzo ya yi nuni da cewa: “Halifofinsa har kiyama ta tashi guda goma sha biyu ne dukkansu daga kuraishi” a wata ruwaya Bani Hashim. Littattafai masu yawa na Ahlussunna da Mabiya mazhabar Ahlul Baiti (A.S) sun kawo har sunayensu wanda ya fara daga Ali (A.S) zuwa Mahadi (A.S) kamar adadin Nakibai na Bani Isra’ila da kuma Hawariyawan Annabi Isa (A.S) kamar haka: Ali Dan Abi Dalib (A.S) HassanDan Ali (A.S) Husaini Dan Ali (A.S) Ali Dan Husaini (A.S) Muhammada Dan Ali (A.S) Ja’afar Dan Muhammad (A.S) Musa Dan Ja’afar (A.S) Ali Dan Musa (A.S) Muhammad Dan Ali (A.S) Ali Dan Muhammad (A.S) Hasan Dan Ali (A.S) sai na karshensu Imam Muhammad Mahadi Dan Hasan (A.S) wanda zai cika Duniya da adalci bayan an cika ta da zalunci. A kowace al’umma wasiyyan annabawa da mabiyansu ‘yan kadan masu tawaye ga halifofi da sarakuna sukanshiga halin wariya da kawar da su gefe guda a tsawon rayuwar duniya, sai ‘yan kadan daga cikinsu da sukan rike jagoranci na wani dan lokaci. A kodayaushe al’amarin shugabanci da iko yakan ci gaba a hannunwadandasuka yi galabaa kan wasiyyan annabawane.
Posted on: Wed, 18 Sep 2013 18:57:48 +0000

Trending Topics



Recently Viewed Topics




© 2015