LABARIN HARIN 11 GA SEPTEMBER A NEW YORK A CIKIN AL-QURANI Ran - TopicsExpress



          

LABARIN HARIN 11 GA SEPTEMBER A NEW YORK A CIKIN AL-QURANI Ran ace da aka saba qullawa musulunci makirci !!! Da sunan Allah wanda ya tseratar da Annabisa daga kisa bayan kulla masa makirci da nufin kisa aranar 11 ga watan Satumba. Kuma dukkan yabo su tabbata ga Allahn da yayi alqawirin samun qalaba ga Imam Mahdi (A.S) bayan harin 11 / 9 watau satumba a karo na biyu. Tsira da aminci ga Annabi Muhammad (S) da iyalansa tsarkaka. Alqawarin Allah na qarshe shine kawar da zalunci da girman kai daga doran qasa, dan maye gurbin su da adalcin sa ta yanda bayinsa zasu kevanta dayi masa bauta ba tare dayi masa shirka ba da kuma yin imani da Annabawansa. Amerika da Isra’ilada ire- irensu , sun kasance masu varna a bayan qasa, alqawarin Allah ne na kawar da zaluncinsu a wata rana. Tabbas Allah (T) ya ambaci labarin NEW YORK a cikin surar Isra’I da, kuma a ka buxa labarin a cikin surar Taubah. Kamar yanda zamu iya gani nan a gaba. An ambaci Kalmar ( ﻭﻋﺪ ﺍﻻﺧﺮﺓ ) sau biyu (2) a cikin surar Isra’I a aya ta (7) da aya ta (104). In muka buga lissafin jumlar ta “wa’adul aakhirati” da qaramin lissafi zamu sami adadin ya kasance (35). Sannan in muka yi sau xin adadin da biyu domin adadin Kalmar (wa’adul akhirati” an maimaita ta sau biyu ne a cikin littafin na Allah (T). 35 x 2 = 70. Sannan in muka sake sau xin adadin (70) sau (19) kamar haka 70 x 19 = 1330. Wannan adadin na 1330 in muka juya shi zuwa qirgan shekarar hjiriyya, zamu samu tayi daidai da 2001. Watau (1 9 11). Wannan adadin shine ya kai mu zuwa ga labarin abinda ya faru a Amerika a ranar 11/9/2001m kamar yanda aka bamu labarin haka a cikin surar Tauba. Surar Tauba ta faxo a Juzu’I na 11 wanda ke alamta mana ranar hujumin da aka kai Amurka. Jerin Surar a Qur’ani shine 9, wanda ke alamta mana watan kai hujumin Hisabin jumla taqlidi zamu sami cewa aya ta 109, da take bada labarin hujumin New York, cewa hisabin ayar zai zama 2001, watau shekarar hujumin. Ajeeeb, labarin New York yazo a tsakaninayoyi 5 watau daga aya ta 107 zuwa aya ta 111. Aya ta 107 tazo da labarin samuwar Masallataida zasu zamazto cutarwa ga Musulunci da Muminai. Hadafin waxannan Mallatai shine kawo rarraba tsakanin Musulmai da raunanasu da kuma Kafirta sashin junansu. Masu Masallatan kuma suna masu rantsuwa da Allah akan cewa su masu kawo gyara ne, alhali Alllah yasan abin da zukatan su suka voye duk da baiyanar akasin abinda ke zuciyoyin su. Waxannan Qungiyo sune qungiyoyi masu kafirta sauran musulman dab a ra’ayin su xaya ba. Kamar Qungiyar BOKO HARAM a Nigeria da cibiyarsu, ire-iren su Alqaa’ida a qarqashin jagoranci shugaban kafirci da qaryatawa da kuma rusawa. Watau Usama bn Ladeen da Aiman Azzawahiriy waxanda suka cutar da Musulunci da Musulmai a duk sassan Duniya, sun vata surar musulunci da Musulmai da kai harin fajirci a Amurka, Spain, Ingila, Iraqi, Kuwaiti da Afganistan da sauran sassan Duniya kamar yanda muke gani daga qaramar qunqiyar tasu a Nigeria watau Boko Haram. Sunyi masallatai dan yaxa tsattsauran ra’ayi da kafirtawa, da sojantar da Matasa da basu mugayen tunani da wahamin su masu Jihadi ne akan tafarkin Allah. A haqiqa wananan lamarin na waxannan munafukan shirine na Yahudu da Nasara da duk wani mai yaqar Addinin Musulunci, sukan hakaito abubuwan cutarwa ga Musulunci ta ciki da ta waje, ta hanyar kafirta duk wanda bai yarda da ra’ayin suba na Jassama ALLAH ( T) wanda wannan tunani ne irin na Yahudu da Nasara. Har wayau suna yaxa agidar cewa Allah wata rana zai sauko Qasa ya zauna a tsakanin mu, wanda hakan ke share fagen yin imani da Masihiddajjal La’ananne a qarshen zamani. Aya ta 108 kuwa tazo da hanine ga Manzo (S) akan tsayuwa a ire-iren waxannan Masallatan. Domin Masallatai ne na cutarwa, kafirtawa da rarraba tsakanin Muminai. Ba a gina su dan ibada ba sai dan tozarta addinin Allah. An siffantasu da marasa tsarki shi kuwa Allah da masu tsarkin zuciya yake shiri. Jama’ar waxannan masallatan zamuga sun duqufa wajen yaqan Musulmai musamman SHI’AH. Yi duba ga abin da ke faruwa a Iraqi da sauran wuraren da Shi’a suke. Aya ta 109 kuwa ta zo da labarin vangarorin gini guda biyu ne. Ginin Imani da taqawa da kuma ginin rashin taqawa da neman yardarm Allah. A qarshe aka siffanta su da zalunci. Aya ta 110 kuwa tayi Magana kan hasara a cikin zukatan Munafiqai, kan gina waxannan masallatan (watau AQIDARSU ta vata) Annabi (S) ya rusa wannan masallacin da aka gina a kusa da Masallacin QUBA’. Sai ga ire- iren su waxannan masallatan mun sake gani akaro na biyu a wannan zamanin suna ta kafirtawa,kawo rarraba a tsakanin Musulmai, da kisan duk wanda baiyarda da aqidarusu ba, sun yaxa wannan aqidar aduk faxin duniya. Hakan zai zo qarshe da baiyanar Imam Muhammad Almahdi (A.S). Aya ta 111 kuwa tazo da maganar Imam Mahdi (A.S) ne da labarinsa yazo a Attaura, Injila da Alqur’ani. Kuma Allah ya sayi rayukan Muminai da dukiyoyin su dan ya basu Aljannah watau waxanda zasu yiqi a qarqashin Imam Mahdi (A.S). Wannan alqawari ne na Allah. Kuma rabauta ne mai girma. Abin mamaki Yahudawa sun san Imam Mahdi (A.S) fiye damu, dalili kuwa shine zuwan su Iraqi domin jiran zuwan sa, sannan kuma su lalata duk wani qarfi da Imam Mahdi (A.S) zaiyi amfani da shi waje yaqan Isra’ila. Amma ga Musulmai sun gafala danga ne da Imamin mu Almadi (A.S). Aleeeeb, Surar Isra’I ana kiranta da Surar Bani Isra’ila, surar tazo da labarin Bani Isra’ila da varnan da zasuyi sau biyu a bayan qasa, da kuma labarin alqawarin Allah na bishe hasken Yahudu, ta hannun Imam Mahdi (A.S). Surar ta Isra’I tana da ayoyi (111), sai ga shi kuma aya ta 111 a Suratu Taubah tazo da labarin nasarar da Imam Mahdi (A.S) zai samu na kawar da zalunci da kwace da suka cika wannan duniyar tamu. Har yanzu ga wani hisabin dangane da Surar ta Taubah, da zai san yanya mu qara gane cewa abin da ya faru a NEW YORK alqawin qarshe ne da labarin sa yazo a Surar ta Taubah. In muka tsayu da hisabin kalmomin aya ta 107 zuwa aya ta 111 a cikin Surar ta Taubah, zamu sami adadin kalma 1911. (a hisabin rubutun qur’ani imla’iy) wan da kuma wannan adadin shine qimar adadin hisabin “WA’ADUL AKHIRAH” Wanda kuma wannan lissafin ne yake kaimu zuwa ga lissafin shekarar hujumin NEW YORK, watau ta hanyar sanya rarrabewa tsakanin alqaluman. Mai karatu da zaka yi sau (x) na 111 da wancan adadin na 1911 zaka sami amsarka ta zama 2022. Kamar haka 111 x 1911 = 2022 wanda ke nuna mana shekarar da Qasar Isra’ila zata rushe. In kuma muka xan koma baya kaxan zuwa aya ta 106 acikin dai surar ta Taubah zamu sami cewa adadin alqaluman ta shine 2014 wanda kuma wannan lissafin shine yakaimu ga shekarar da Tauraruwa maiwutsiya da zata rigayi zuwan Imam Mahdi zata baiyana. Haryanzu in muka yi sau (x) na adadin wancan ayar ta 106 ta cikin Surar Taubah da 19 amsar za ta fidda 2014, kamar haka ; (106 x 19 = 2014 ). Kuma wannann lissafin shine ya kaimu ga shekarar AZABAR da ayar ta 106 ta cikin Taubah take magana akan Larabawa. Ayoyi goma (10) kafin labarin NEW YORK, sun bamu siffa da xabi’un larabawa. Wautau daga aya ta 97 zuwa aya ta 106 kenan. Wannan azabar zata mamayi yankin Larabawa, domin ita wannan Tauraruwar zata share fagen zuwan Imam Mahdi (A.S) ne. Domin faruwar aya mai bantsoro da firgitarwa zai sanya mutane su dawo cikin haiyacinsu, domin yin abinda zai zame masu alheri. Imam Sadiq (A.S) ya bamu labari da cewa “Baiyanar Tauraruwa mai wutsiya zata firgita Larabawa, wani Tauraro ne ta vangaren Gabas da haskaka kamar hasken wata, zai kusa ya hadu da duniya , Jan haske zai cika sararin sama da sassan duniya.” Ya mai karatu in ka tafi zuwa qirgan Surorin Alqur’ani za kami Surar Quraishu it ce Sura ta 106 a cikin jerin surorin Alqur’ani. Wanda hakan ke qara nuna mana al’amarin Lrabawa. In muka koma ga Tauraruwa mai wutsiya da zata baiyana a 2014m, zamuga cewa Ahlulbait (A.S) sun bamu labarin gittawar Tauraruwa mai wutsiya ta birbishin sararin samaniyar yankin Larabawa ta bangaren Iraqi ta saman KUFA, SUNCE Kogin FURAT zai tumbatsa har sai yashiga Kufa. Dubi wannan hoton danganin yanda wannan tauraruwar zata gitta wannan duniyar tamu. Ya mai karatu adadin alqaluman 11 ya bamu labarin Amekrika ta wurare da yawa kamar yanda zan baiyana mana yanzu. 1 . Yaqin ‘yanta Kuwait da Amerika ta jagoranta ya kasan an fara shi aranar 11/1/1411. 2. Amurka ta shiga yaqi a Iraqi a shekara ta 1424 ( 1 + 4 + 2 + 4 = 11). 3. Ginin Tagwayen Benayen kasuwancin duniya ya kasance a gini na 11. 4. Ranar Hujumin ta kasance rana ta 11. 5. Sannnan harin ya kasance a ranar 11/9 ( 1 + 1 + 9 = 11). 6. Ranar 11 ga Satumba ita ce rana ta 254 a lissafin girgan shekarar Miladiyah. ( 2 + 5 + 4 = 11 ). 7. Bayan 11 ga Satumba sauran kwanakin da suka rage ma shekarar sune kwanaki ( 111). 1 x 11 = 11. 8. Adadin haruffan kalmar NEW YORK CITY sune haruffa 11. 9. Kalmar BUSH da aka kai harin a zamanin sa ya kasance 11. 10. Kalmar AMERIKA tayi daidai da 11. 11. Amerika ta baiyana amincewarta da qasar Isra’ila bayan mintuna 11 da aiyanata. 12. BUSH ya ziyarci Iraqi a cikin sa’o’I 11. Shin ko saukowar Annnabi Almasihu (A.S) zai kasance a ranar 11/9/2018m, daidai da 1/1/1440h da ta dace da ranar TALATA. Allah ne masani. Kar ka gaji ya kai mai karatu, ga wani binciken dangane da wannnan lissafin na (1911), da take misalta mana shekarar farko da Amurka ta fara yaqar Imam Mahdi (A.S). Ga binciken kamar haka: Italiya ta ‘yanta LIBIYA a shekara ta 1911. Faransa ta ‘yanta MOROKO a shekara ta 1911. An haifi shugaban Amurka RONALD REGAN A a shekara ta 1911. Wannnan lisafin da shine farkon farawar kutsen qasashen yamma ga qashen Larabawa, gami da gudummuwar qasar Rasha. Wannan lamarin na ( 11/9/2001 ) zai ci gaba har tsawon shekaru n adadin Ma’asuma ko kuma adadin A’immah daga shigar Amerika Iraqi. In muka yi nazari kan karairayin da aka yaxa dangane harin na ranar (11/ 9 /2001 ) za muga cewa shine mafi munin qarya da Duniya ta ji a dukkanin tarihin Xan’adam. Hadafin wannan harin shine zare takobi akan Musulunci da Musulmai, a duk sassan Duniya. Waxana qarairayin sun baiyana qarara kuma sun yaxu a shafin YOUTUBE a Intarnet . Abin tambaya anan shine da wani dalili ne yasanya suka xauki wannan rana ta 11/ 9 dan gudanar da wannan aikin??? Amsa anan ita ce, tarihin wannan rana ta 11/9 ya kasance ranar rundunar Kafirci suka zare Takubba akan Rasulul A’azam (S), a shahararren labarin daren Hijira, da Imam Ali (A.S), ya kwana akan shimfixar Ma’aiki (S). Wannan taron gangami dan kashe ANNABIN RAHAMA da MUSULUNCI a cikin darun Nadawa da dattijan Larabawan Makka 40 sukayi gami ta tallafin na 41 watau Tsohon Najadu (IBILIS La’ananne), ya kasance ne a ranar Asabar 11 /9 /622 m. Wacce tayi daidai da 29 /2 / 1 h. A zatonsu in Annabi (S) yayi barci su gama dashi. Allahu Akbar Allah ya tseratar da Annabinsa ya kuma kunyatar da kafirai da Kafici da samun dama da Nasarar kafa Gwannatin Muslunci a Garin Madina bayan kwanaki 12 da yin taron gangamin murqushe Annabi (S) da Musulunci. Kwanaki 12 suna alamta mana khalifofin da zasu khalifaci bayan Annabi (S). A karo na biyu IBILIS (L) ya sake dawowa aranar Talata 11 /9 /2001m da yi daidai da (23 /6 1422 ), in da ya haxu da ‘Yan ‘uwan sa Shaixanu da wasu vangare na Quraishu (watau ‘ALQA’IDAH). Suka zare Takubban su dan yaqar Imam Mahdi da Annabi Isa (A.S). Dalin yin haka gabaxaya shine dan kusantowar “waqatil ma’alum” ta baiyanar mai ceton duniya bayan cikata da zalunci da fin qarfi, da Ibilis da Shaixanun Azzaluman mataimakansa. A qarshe Imam Mahdi (A.S) zaiyi nasarar shimfixa DAULAR ADALCI bayan shekarun da Annabi (S) ya kwashe dan wanzar da saqon Musulunci watau shekaru 23 daga harin na 11 /9 /2001 ga lissafin a cin tarihin kai harin na NEW YORK CITY kamar haka ( 11 + 9 + 2 + 0 + 0 + 1 = 23 ). Ibilis ya bada shawarar dabarar kashe Annabi (S) akan shinfixar sa in yayi barci. A karo na biyu Ibilis ya dawo a irin wannan ranr ta 11 / 9, da tunanin Ibilis da shaixanun Mataimakansa a kan cewa Musulunci yayi barcin da ba zai tashi ba. Saidai kash Allah zai kunyatar dasu . Haqiqa dukkan Labarai muhimmai da sukazo da labarin baiyanar Imam Mahdi, da sukowar Almasihu Isa xan Maryam (A.S) da kuma adadin shekarun Isra’ila, duk suna rubuce a farkon ayar da ta buxe farkon Sura daga Surorin Alqur’ani, wacce ta ke xauke da ayoyi 7, Watau “ BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM “. In mukayi duba ya zuwa wannan ayar ta BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM zamu sami iya sauqi dangane da haihuwar Imam Mahdi (A.S). Kamar yanda Imam Ali (A.S) ya ambata da cewa: “Idan zamani ya kewaya adadin haruffan “ BISIMILLH “ to Mahdi zai tsayu, a qarshe yake cewa duk wanda ya riski lokacin ya isar masa da gaisuwarsa ga Imam Mahdi (A.S). Kalmomin “ BISMIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM ” sun ginu a bisa kalmomi huxu (4), da suka ginu akan haruffa goma sha tara (19). Idan mukayi sau ( x ) na adadin haruffan 19 da na adadin kalmomin BASMALA guada 4 zamu sami adadin ya zama 76 kamar haka: ( 19 x 4 = 76 ). Wannan adadin na 76 shine kuma adadin shekarun da qasar Isra’ila za tayi a karo na biyu na fajircin su. Sannan in mukayi sau ( x ) na adadin da muka samu watau 76 da 19 adadin zai zama kamar haka ( 76 x 19 = 1444). Wannan adadin shine na shekarar da Imam Mahdi (A.S) zai jagoranci al’ummar Musulmai shiga Qudus domin ‘yantar da ita. Sannan kuma in muka sake yin sau ( x ) da adadin da muka samu na 1444 da adadin kalmomin Basmala 4 za mu taras da sakamakon kamar haka: 1444 x 4 = 5776 , wannan adadin lissafin shine zai komar damu qirgan shekarar Yahudu da muke sa ran baiyanar Imamul hujjah (A.S). Shekarar 5776 ita ce tayi daidai da 2015m daidai kuma da 1437h. Har yanzu dai ya xan’uwan da zakayi sau ( x) na adadin haruffan BASMALA 19 sau 4 dana adadin kalmomin na BASMALA kamar haka ( 19 x 4 x 4 = 5776 ). In kuma muka xebe ( - ) 4 cikin adadin 1444 kamar haka ( 1444 - 4 = 1440 ), wacce zata kaimu zuwa ga shekarar da muke sa ran sakkowar Annabi Isa (A.S). watau 2018m. In muka sake xebe ( - ) 4 cikin adadin 2018 sakamakon zai zama kamar haka: 2018 – 4 = 2014, wacce it ace shekarar da zata share fagen baiyanar ta Imam Mahdi (A.S) . Shekarar da za a sami rowan sama mai tarin yawa. Kar ka gaji ya mai karatu sake xebe 7 na adadin ayoyin surar Fatiha a cikin adadin 1444 zaka sami natijar ita ce 1437 kamar haka ( 1444 - 7 = 1437 ) wacce tayi daidai da shekarar 2015m. Ga wani abin lura shekarar Yahudu ta 5776 ita ce tayi daidai da 1444 sau 4, kamar haka ( 1444 x 4 = 5776 ). Kenan hakan na nuni da cewa shekarun Yahudu ya nunka na Hijiran Musulunci har sau 4 kamar haka: ( 1444 + 1444 + 1444 + 1444 = 5776 ) . An bamu labarai a cikin Surar Isra’I cewar qasar Isra’ila a karo na biyu zata wanzu na tsawon shekaru 76 da kafuwar ta da yakasance a ranar (14 / 5 / 1948M. daidai da 1367H kuma 5708 a kalandar Ibriy ), da zata qare da baiyanar Imam Mahdi (A.S). In mukayi ( x) na adadin 76 sau biyu amsar it ace kamar haka (76 x 76 = 5776 ) wacce tayi daidai da 2015m. Kenan shekarar 5776 ita ce skararar da zata zama saura shekaru 7 qarshen YAHUDU ta kasance, ta hanyar tsarkakewar da Imam Mahdi (A.S) zaiyi ga qasar Qudus, kenan Imam Mahdi (A.S) zai wanzu a tsakanin mu na tsawon shekaru 7 kafin ‘yanta AL’AQSA. Labarin cikin mamaki a bisa yanda Yahudu ke tsanani gaba da adadin (7 ), domin sun san cewa qarshen su zai kasance a wannan adadin na ( 7). 76 × 76 = 5776 × 19 4 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 1444 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 1444 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 1444 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 76 1444 Via...............Muhammad Sani Ra’is Funtua. 0703 459 5991. 0805 983 0178.
Posted on: Wed, 11 Sep 2013 15:08:27 +0000

Trending Topics



Recently Viewed Topics




© 2015