TUSHEN ZUNUBAI GUDA UKU NE 1. Girman kai: wanda shi ne ya kai IBLIS zuwa kin yin sujjada ga Annabi Adam lokacin da Allah ya umarce shi. 2. Kwadayi: wanda shi ne ya fitar da Annabi Adam daga Aljanna, a lokacin da ya ci bishiyar da Allah ya hana shi. 3. Hassada : wadda ta sa daya daga cikin yayan Annabi Adam ya kashe danuwansa. Duk wanda aka kare shi daga wadannan abubuwa guda uku, to an kare shi daga sharri, domin KAFURCI daga GIRMAN KAI yake, SABO daga KWADAYI yake, ZALUNCI daga HASSADA yake. Idan muka kula za ka ga su ne farkon zunuban da aka sabi Allah da su, don haka sai mu guje su. Yaa Ubangiji Ka Nesanta Tsakaninmu da wadannan Zunuban,Ka Tsarkake Zukatanmu DAGA KOWANNE IRIN DATTI na sabonka Yaa Allah.
Posted on: Tue, 03 Dec 2013 10:51:51 +0000