YI KOYI DA WANNAN MATA DA MIJIN. Ina kara mika godiyata ga mijina, domin a yanzu ya zama garkuwa a gare ni, ya zama madagora a gare ni, ya zama ginshiki a gare ni, ya kuma zama wani sinadari da ke sanya rayuwata armashi. Mijina yana taimaka mini wurin lura da yara, ya yi musu wanka, yana taimaka mini a kicin, inda idan ba ni da lafiya ko ma ina da lafiya yakan shiga kicin ya girka mana abinci. Ranar Asabar ko Lahadi idan yana gida tare muke share gida, mu wanke bandaki, mu gyara falo da dakin kwananmu, mu yi dukkan aikace-aikacen gida. Allah Ya saka masa da alheri.” Wannan ne ya tabbatar mini tattaunawa tsakanin ma’aurata na da matukar mahimmanci, za ta kuma inganta hade da kara dankon aure. Don haka nake fatan ma’aurata da kuma wadanda za su yi aure gaba su yi amfani da darussan cikin labarin nan. Allah Ya taimake mu, amin. Muhsin
Posted on: Fri, 22 Nov 2013 04:39:04 +0000