Masu sauraro Mustapha Muhammad ne yake muku barka da safiya. A cikin shirin namu na 6:30am za ku ji matakan da kasar Saudiyya ta fara dauka kan bakin haure dake kasa bayan waadin da aka debarwa yan ci rani dake aiki a kasar. Haka kuma Kungiyar ASUU da Gwamnatin Najeriya sun shafe daren jiya suna tattaunawa kan yajin aikin da yan Kungiyar ke yi, zaku ci karin bayani kan abin da ya faru. A Jamhuriyyar Nijar kuwa an ceto was mutane ne yan ci rani kusan sabain mata da kananan yara wadanda suka makale a Sahara bayan motar su ta lalace. Ku biyo mu don jin shirin wanda Abba Mohammed katsina zai gabatar in sha Allah.
Posted on: Tue, 05 Nov 2013 03:20:55 +0000